in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bayani kan abokinmu dan kasar Canada Bethune
2010-11-23 15:20:08 cri
Masu karanta, muna fatan kuna cikin koshin lafiya kamar yadda muke a nan birnin Beijing. Kamar yadda muka saba, a cikin shirinmu na yau, da farko bari mu karanto wasu wasikun da muka samu daga wajenku. Ga wannan sako daga malam Nuraddeen Ibrahim Adam a Kano, tarayyar Nijeriya, inda ya rubuto mana cewa, "Na karanta wani labari a shafinku na yanar gizo a ran 16 ga wata dangane da labarin da aka samu daga hukumar 'yan kasuwan Nijeriya ta kamfanin Haier na kasar Sin cewa, a cikin takardar jerin sunayen gasar neman kwangilar na'urorin yin rajistar sunayen masu kada kuri'a na zaben shugaban kasar Nijeriya na shekarar 2011. Wato yanzu, kamfanin Haier na kasar Sin ya lashe wasu kamfanonin kasashen waje ke nan, kuma shi zai samar wa Nijeriya Computar tafi-da-gidanka dubu 30. Kamar yadda na karanta, kamfanin Haier ya yi fice, domin ya zama zakaran sauran kamfanonin ketare da suka nemi samar wa Nijeriya na'urorin kidaya kuri'un masu zabe, da ya hada da kamfanin HP, Dell, Acer, Lenovo, da Samsung da dai sauransu. Lalle wannan nasara da kamfanin Haier ya samu, ta zama wata babbar shaida dake tabbatar da ci gaban da ya samu a fannin kirkire-kirkire. Ra'ayina dangane da wannan labari shi ne, kasar Sin bisa kokarin kamfanin Haier za ta taimaka wa kasar Nijeriya ke nan wajen kidaya kuri'un masu zaben shugaban kasa a shekarar 2011 cikin inganci, wanda hakan zai ba da damar samun sakamakon zabe mai nagarta da sahihanci."

To, mun gode, mai sauraronmu a kullum malam Nuraddeen Ibrahim Adam. Mu ma muna farin ciki sosai da wannan labari. Kamfanonin kasar Sin suna kokari sosai wajen tabbatar da ingancin kayayyakin da suke samar. Muna fatan wadannan kamfutoci da kasar Sin za ta samar za su ba da taimako a cikin babban zaben kasar Nijeriya a shekarar 2011 yadda ya kamata. Da fatan za a gudanar da zaben lami lafiya.

Sakon malam Nuraddeen Ibrahim Adam ke nan. Bayan haka, malam Bello Gero a Sokoto, tarayyar Nijeriya ya bayyana mana cewa, "Ina mai matukar nuna farin cikina zuwa ga dukkanin ma'aikatan sashen hausa na CRI don gane da kulawarku a gare ni da kuma iyalina. Ina mai sanar da ku cewa, yarinyar da aka haifar mini tana nan lafiya lau, kuma an rada mata suna Halimatu Sadiya. Tana nan cikin koshin lafiya tare da mahaifiyarta da kuma sauran iyali baki daya. Bayan haka, nan ba da dadewa ba, za ku sami hotonta idan Allah ya so ya yarda."

To, malam Bello Gero, muna taya maka murna sosai da sosai. Kuma muna fatan ganin hoton diyarka cikin sauri, ko shakka babu, za ta yi kyan gani kwarai da gaske. Da fatan za ta girma lami lafiya, tare da farin ciki.

Sakon malam Bello Gero ke nan. A makon jiya, malam Adamu Issa a Kano, tarayyar Nijeriya ya yi mana tambayar cewa, "Don Allah ko za ku ba da wani bayani dangane da Norman Bethune?" To, malam Adamu Issa, yanzu za mu kokarta amsa wannan tambaya, da fatan kana sauraronmu.

An haifi Norman Bethune a shekarar 1890 a garin Gravenhurst na jihar Ontario ta kasar Canada. Ya kammala karatunsa a kwalejin ilmin likitanci na jami'ar Toronto a shekarar 1916. Daga bisani, an zabe shi a matsayin memba na majalisar likitancin kirji a shekarar 1935. Ya yi suna sosai a sashen likitanci na kasar Canada, Birtaniya da Amurka. A watan Nuwamba na wannan shekara, ya shiga jam'iyyar kwaminis ta kasar Canada.

Bayan abkuwar yakin Spainiya a shekarar 1936, ya jagoranci wani rukunin likitoci zuwa Madrid domin ba da jiyya ga jaruman sojoji masu yaki da Fasist. A shekarar 1937, yaki da hare-haren sojojin Japan a Sin ya barke. Bethune dake samar da kudi ga yakin Spainiya a Canada da Amurka ya yi jawabi cewa, "Ana hakikanin yaki a kasar Sin, wanda zai tabbatar da makomarmu baki daya. Dole ne na yi gwagwarmaya tare da su!"

A watan Janairu na shekarar 1938, bisa umurnin jam'iyyar kwaminis ta kasar Canada da ta Amurka, Bethune ya jagoranci wani rukunin likitocin Canada da na Amurka tare da na'urori da dama zuwa kasar Sin, domin ba da taimako ga jama'ar kasar. Bayan shan wahalhalu da yawa, a karshen watan Maris na shekarar 1938, Bethune ya isa Yan'an, inda Mao Zedong ya yi maraba da zuwansa, tare da nuna babban yabo ga ziyararsa a Sin domin ba da agaji. Daga bisani Bethune ya je fagen yaki nan take. A cikin shekaru 2 a lokacin, Bethune ya yi aiki matuka tare da sadaukar da kansa domin ba da jiyya ga sojojin JKS.

A kokarin kyautata yanayin kiwon lafiya a yankin yaki da sojojin Japan, Bethune ya ba da shawarar kafa kamfanin samar da kayayyakin kiwon lafiya, a kokarin daidaita matsalar karancin magunguna. Kuma ya ba da kos na koyar da ilmin likitanci, tare da kafa dakuna da rumfunan ba da jiyya 13 ga rundunar sojan Jizhong. A watan Yuni na shekarar 1939, bayan da ya koma yankin Jixi, Bethune ya kafa makarantar kiwon lafiya, ya tabbatar da kos da kansa, tare da rubuta littattafai kimanin 20. Ya yi aiki matuka. A cikin wasikar da ya aika wa abokinsa na Canada, ya rubuto cewa, "Lallai ina gajiya sosai. Amma ina farin ciki kwarai, sabo da ana bukatar taimako da nake bayar sosai."

A karshen watan Oktoba na shekarar 1939, yayin da yake ba da jiyya ga sojoji da suka ji rauni a gundumar Laiyuan ta lardin Hebei, daya daga cikin yatsunsa na hannun hagu ya raunata. Amma bai ta da hankali ko kadan ba. Ya ci gaba da aikinsa har tsawon rayuwarsa. A ran 12 ga watan Nuwamba na shekarar 1939, Bethune mai shekaru 49 da haihuwa ya rasu a kauyen Huangshikou dake gundumar Tang ta lardin Hebei na Sin.

A ran daya ga watan Disamba na wannan shekara, sassa daban daban na Yan'an sun gudanar da bukukuwan tunawa da likita Norman Bethune.

A watan Disamba na shekarar 2009, a cikin wani aikin da gidan rediyon kasar Sin da hukumar sada zumunci a ketare ta jama'ar kasar Sin, da hukumar kula da kwararrun ketare ta kasar suka shirya, Norman Bethune ya zama daya daga cikin abokanmu na kasashen waje guda 10 da suka fi sada zumunci a kasar Sin.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China