in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yadda kungiyar IS ke lalata kayayyakin tarihi
2015-04-26 15:39:17 cri

A kwanakin baya ne kungiyar IS mai da'awar kafa daular musulunci ta lalata kayayyakin tarihi da dama a dakin adana kayan tarihi na Mosul da ke kasar Iraki da kuma tsohon birnin Nimrud.

Kasashen duniya da hukumomin kasa da kasa ciki har da hukumar kula da harkokin yawon shakatawa da kayayyakin tarihi ta Iraki sun yi allah wadai da yadda 'yan kungiyar IS suka lalata tare da sace kayayyakin tarihi masu daraja na tsohon birnin Hatra har ma da lalata birnin.

Birnin Hatra mai tazarar kilomita 70 daga garin Mosul da ke kudu maso yamma kasar Iraki ya taba zama muhimmin sansanin soja na daular Parthia da hedkwatar daular Larabawa ta farko. A shekarar 1985, kungiyar UNESCO ta sanya shi cikin jerin wuraren kayayyakin tarihi na duniya.

Kungiyar UNESCO ta bayyana cewa, kungiyar IS ta aikata laifin yaki a sakamakon lalata kayan tarihi da gangan, yayin da babban sakataren MDD Ban Ki-moon shi ma ya soki wannan danyen aiki da babbar murya, inda ya ce, kungiyar ta aikata laifin yaki sakamakon yadda ta lalata kayayyakin tarihi na dan Adam baki daya kuma wannan tamkar hari ne da ta kai wa duk kan bil'adam.

Masharhanta na cewa, wannan danyen aiki na kungiyar IS kan muhimman kayayyakin tarihi mayar da hannun agogo baya ne a kokarin da hukumomi da gwamnatoci ke yi na kiyaye tarihi da abubuwan gado na kaka da kakanni daga bacewa daga doron kasa. Don haka wajibi ne a dauki mataka da suka wajaba na kiyaye wadannan muhimman abubuwa da ke bayyana tarihin rayuwar bil-adam. (Ibrahim/Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China