in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Matsayin kasar Rasha da kasashen yamma kan rikicin Sham
2015-10-15 16:31:29 cri

A ranar 30 ga watan Satumban shekarar 2015 ne sojojin saman kasar Rasha suka kaddamar da hari kan sansanonin 'yan ta'adda a kasar Syria, inda ta bayyana cewa, tana kai hare-hare a Syria ne domin yaki da 'yan ta'adda tare da kawo daidaito a halaltacciyar gwamnatin Bashar al-Assad.

Shugaba Putin na Rasha ya ce, hare-haren da dakarunsa ke kaiwa kan 'yan ta'adda, zai taimaka wajen samar da yanayin da ya dace ga 'yan siyasar kasar Syria ta yadda za su yi bani-gishiri-in-baka manda.

Kasashen yammacin duniya karkashin jagorancin Amurka na adawa da matakan soja da Rasha ke dauka a Syria. Ma'aikatar tsaron Amurka ta bayyana cewa, sojojinta za su dakatar da shirinsu na horas da kungiyar 'yan adawar kasar Sham, inda za a maye gurbin shirin ta hanyar tallafa musu da makamai domin yakar mayakan kungiyar IS.

Masana a harkar tsaro na ganin cewa, dari-darin da Amurka ke yi game da musayar bayanan sirri game da Syria ba zai kawo wani cikas ga matakan sojan da Rasha ke dauka a Syria ba.

Masu fashin baki na cewa, matakin Amurka da kawayenta kan Syria ba zai rasa nasaba da wata boyayyar manufa kan Syira ba, wanda kuma ya sabawa kokarin hada kan 'yan Syria na kawo karshen rikicin kasar da ya yi sanadiyar dubban rayukan jama'a. (Ibrahim/Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China