in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kanu Nwanko ya ci kwallaye a wasan karrama 'yan wasan kungiyar Arsenal
2016-09-07 19:19:07 cri
Tsohon dan wasan gaban kungiyar kwallon kafar Arsenal, kuma tsohon kyaftin din Super Eagles ta Najeriya Nwankwo Kanu ya zura kwallaye uku a ragar AC Milan Glorie, a wasan karrama tsaffin 'yan wasan kungiyar ta Arsenal da aka buga a filin wasa na Emirates, ranar Asabar din karshen mako.

Kanu wanda yanzu haka ya kai shekaru 40 da haihuwa ya nuna bajimta a wasan, wanda aka tashi Arsenal na da kwallo 4 Milan Glorie kuma na da 2.

Duk da kasancewar ya shiga wasan bayan kusan rabin sa'a da take leda, Kanu ya gwada irin basirar da yake da ita a wasan tamaula, inda ya zura kwallon sa ta farko jim kadan da shigar sa wasan.

Da yake bayyana irin farin cikin sa bayan kammala wasan ta shafin yanar gizon kungiyar, Kanu ya ce wasan ya sanya shi nishadi, duba da yadda ya ba shi damar taka leda da kuma faranta ran 'yan kallo da masu goyon bayan kungiyar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China