Masu aikin ceto sun bayyana cewa, yanzu haka an gano gawawwaki 5 a dab da jiragen ruwan, wadanda shekarunsu ke tsakanin 16 zuwa 25.
Kungiyar dai ta bayyana cewa, ko wane jirgin ruwa irin wadanda aka gano na daukar 'yan gudun hijira fiye da 120, don haka mai yiwuwa ne wasu mutanen fiye da 250 sun bace a sakamakon hadarin. Kuma da yake hadarin ya faru sama da kwana guda, akwai yiwuwar samun karin wadanda suka rasu sakamakon hadarin.
Ofishin kula da harkokin 'yan gudun hijira na MDD ya nuna matukar juyayi da aukuwar wannan lamari. (Zainab)