in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babbar kotun Amurka ta sassauta daskarar wasu jimlolin umurnin gwamnatin Trump na kayyaden baki daga ketare
2017-06-27 09:53:34 cri
A jiya Litinin, babbar kotun Amurka ta amince da umurnin gwamnatin Trump na kayyade baki da za su kaura daga ketare, tare da bayyana cewa, za ta yanke hukunci kan ko wannan umurni ya dace da doka ko a'a a watan Oktoban bana.

A wannan rana, babbar kotun Amurkar ta bayyana a wata takardar doka cewa, ta amince da yanke hukunci kan ko umurnin kayyaden baki da za su kaura daga ketare ya dace da doka ko a'a, kuma ya amince da sassauta hukunci da kotun tarayyar kasar Amurkar ta yanke na daskarar da wasu jimlolin umurnin nan take.

Bisa wannan takardar doka, umurnin ba zai kayyade wadanda ke da ainihin alaka da mutane ko kungiyoyi a Amurka wajen shiga kasar ba, yayin da zai kayyade wadanda ba su taba zuwa Amurka ba kuma ba su da dangi da sauran wata alaka da kasar wajen shiga kasar ta Amurka.

Ko da yake wannan takarda ta bayyana ra'ayin babbar kotun Amurka, amma ba tare da sa hannun manyan alkalai ba. Bisa labarin da kafofin yada labarai na Amurka suka bayar, an ce, a kalla manyan alkalai uku sun nuna rashin amincewa kan batun, a ganinsu, kamata ya yi a sassauta daskarar umurnin duka. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China