Lu Kang ya ce shugaba Xi zai kai ziyara wadannan kasashen ne bisa gayyatar takwarorinsa na kasashen Rasha Vladimir Putin da na Jamus Frank-Walter Steinmeier da kuma shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel.
Ana kuma saran shugaba Xi zai halarci taron kolin kasashen kungiyar G20 da zai gudana a birnin Hamburg na kasar Jamus daga ranar 7 zuwa 8 ga watan Yuli. (Ibrahim)