Hare-hare ta sama sun hallaka kusan mutane 100 a Syria
Kamfanin dillacin labarai na kasar Syria ya ba da labari a jiya Talata cewa, cikin kwanakin da suka gabata, kawancen kasa da kasa dake karkashin jagorancin kasar Amurka, ya yi ta kai hare-hare ta jiragen sama kan dakarun IS masu tsattsauran ra'ayi dake cikin kasar, sai dai a lokaci guda hare-haren sun yi sanadiyyar mutuwar jama'ar kasar kusan dari daya.(Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku