in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sudan ya lashi takobin kakkabe makamai daga yankin Dafur
2017-08-24 10:07:28 cri
Shugaban kasar Sudan Omar Al-Bashir, ya lashi takobin daukar matakin karbar makamai a matsayin babban abun da ya sanya gaba a yankin Dafur, ya na mai gargadi game da tasowar matsalolin tsaro a yankin.

Omar Al-Bashir ya jadadda cewa, Gwamnati ba za ta lamunci tashin matsalolin tsaro a Dafur ba.

A jiya Laraba ne Shugaban ya gana da Gwamnan Dafur ta Arewa Abdulwahid Yousif, kuma yayin ganawar ne, Gwamnan ya shaidawa shugaban bukatar ci gaba da karbar makamai a matsayin matakin kawar da makamai baki daya daga yankin Dafur.

Shugaban kasar ya umarci Gwamnan ya ci gaba da tabbatar da tsaro da zaman lafiya da aka samu a yankin.

Har ila yau, Omar Al-Bashir ya umarci Gwamnan ya tsugunar da 'yan gudun hijira tare da maganace matsalolin tsaro da na jin kai.

A ranar 7 ga watan nan ne Gwamnatin Sudan ta kaddamar da gangamin karbar makamai a yankin Dafur. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China