Wannan shi ne zagaye na 8, na tattaunawar neman sulhu a Syria da MDD ke jagoranta.
Babu wani tsokaci da ya fito daga wakilan Gwamanti karkashin jagorancin wakilin kasar a MDD Bashar al Jaafari game da tattaunawar da suka yi da manzon na MDD. Sai dai, bangaren adawa sun yi ikirarin cewa, akwai wata dama a tattaunawar ta wannan mako, da ya zama dole su yi amfani da ita domin al'ummarsu.
Bangaren adawar dai, ya tsaya kai da fata kan matsayinsa dake neman sai shugaban kasar Bashar al-Assad ya sauka daga mulki, a matsayin sabon babi na tsarin siyasa, wanda kuma Gwamnati ke ganin ba mai yuwa ba ne, tun da dakarunta sun kwace iko da muhimman yankunan kasar daga hannun 'yan tawaye.
An shirya cewa, sabon zagayen tattaunawar neman zaman lafiya a Syria da MDD ke jagoranta da aka fara a ranar 28 ga watan Nuwamba, zai ci gaba da gudana har zuwa ranar 15 ga watan nan na Decemba. MDD ta bayyana rashin aminta da juna a matsayin babban tarnakin dake hana samun nasarar tattaunawar. (Fa'iza Mustapha)