in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Sin ya baiwa daliban jami'ar ABU kyautar kudin karatu
2018-02-13 10:27:33 cri




A kwanakin baya ne, jakadan Sin dake Nigeria Mista Zhou Pingjian ya ziyarci jami'ar ABU dake jihar Kaduna, inda ya baiwa daliban jami'ar 47 kyautar kudin karatu.

Jakadan ya kuma bayyana cewa, wannan shekara, shekaru 47 ke nan da kulla dangantakar diplomasiyya tsakanin Sin da Nigeria, shi ya sa a wannan lokaci mai muhimmanci na tunawa da wannan dangantaka,kasar Sin ta baiwa wadannan dalibai 47 wannan kyauta ta yadda bangarorin biyu za su habaka hadin gwiwar dake tsakaninsu.

Mista Zhou ya kuma tabo batun taron kolin dandanlin hadin gwiwar Sin da Afrika da za a yi a birnin Beijing a watan Satumba wannan shekara, inda ya ce matasa sune kashin bayan kowa ce kasa, kuma kulla zumunci da dalibai zai taimaka sosai wajen habaka hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu nan gaba.

Wakiliyarmu Amina dake Nigeria ta hakarci biki ta kuma zanta da malam Ibrahim Garba shugaban jami'ar ABU, wanda ya bayyana muhimmancin kyautar kudin karatu.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China