Da yake tsokaci game da shirin da ake yi, na halartar shugaban kasar Rasha taron na SCO, Mr. Geng ya ce Sin za ta sanya sabon kaimi ga ci gaban kungiyar, tana kuma maraba da zuwan sabon shugaban na Rasha, duba da irin kimar da kasar ke da ita a kungiyar.
Ana dai sa ran gudanar da taron SCO ne a birnin Qingdao cikin watan Yuni na wannan shekara. (Saminu Hassan)