Wata sanarwa da kakakin rundunar sojin Nijeriya Sani Kukasheka ya fitar, ta ce rijiyar kari ne akan ayyukan gyaran tituna da ake yi domin samar da kayayyakin more rayuwa a dajin da ma al'ummomin yankin.
Sani Kukasheka ya ce an tona rijiyar ne domin samar da ruwa ga dakarun da sauran al'ummomin yankin, a wani yunkuri na kyautata yanayin rayuwa a dajin
A cewarsa, aikin wani bangare ne na kakkabe ragowar mayakan Boko Haram.
Sani Kukasheka ya kara da cewa, rundunar ta tona rijiyar ne a sansanin 'yan ta'addan na Sabil Huda dake dajin bayan ta fatattake su, domin samar da ruwan sha mai tsafta ga dakarunta. (Fa'iza Mustapha)