in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane miliyan 10 ne ke bukatar tallafin abinci saboda yadda ake tsaka da fama da fari a yankin sahel
2018-04-21 16:10:35 cri

MDD ta ce karancin ruwan sama a bara ya haifar da fari da ya shafi galibin yankin Sahel, al'amarin da ya jefa mutane sama da miliyan 10 cikin tsananin bukatar abinci a bana.

Kakakin MDD Farhan Haq, ya ruwaito ofishin hukumar dake kula da agajin jin kai na cewa, tuni lokacin bazara dake kai wa har watanni Yuni da Augusta, ya fara tun a watan Maris a wasu yankunan, wanda ya haifar da asarar dabbobi. Abun da ya haifar da matsala fiye da yadda aka saba gani musammam a yankunan da ake kiwo da wadanda ake noma da kiwo.

A cewarsa, baki daya dai, sama da mutane miliyan 10 ne za su bukaci agajin gaggawa na abinci a lokacin bazara, adadin da ya karu kan miliyan 7.1 da ake da shi a yanzu.

Bugu da kari, ya ce yara miliyan 1.6 'yan kasa da shekaru 5 ne ke fama da matsananciyar tamowa, adadin da ya karu kan na bara da kaso 46.

Matsalar ta fi kamari ne a kasashen yankin Sahel da suka hada da Burkina Faso da Senegal da Chadi da Mali. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China