in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Koriya ta Arewa ta dakatar da gwajin makaman nukiliya da na harbar makamai mazu linzami
2018-04-21 16:11:52 cri
Kamfanin dillancin labaru na KCNA na kasar Koriya ta Arewa, ya ruwaito a yau Asabar cewa, kasar ta tsaida kudurin dakatar da gwajin makaman nukiliya da harbar makamai masu linzami daga yau Asabar 21 ga wata.

Gwamnatin kasar ta tsaida wannan kudurin ne yayin cikakken zama na 3 na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwadago ta kasar karo na 7 da ya gudana a jiya Jumma'a.

KCNA ya kuma ruwaito cewa, ban da wannan, an kuma zartas da wasu matakan da suka hada da rufe filin gwajin makaman nukiliya dake arewacin kasar don tabbatar da dakatar da gwajin makaman baki daya.

Kudurin ya kara da cewa, kasar ba za ta yi amfani da makaman nukiliyar ba muddun ba ta fuskanci barazana ba. Sannan, Kasar ba za ta mika makaman nukiliya da fasahohinta ga kowa ba.

Har ila yau, an tsaida kudurin cewa, za yi amfani da albarkar jama'a da kasar ke da su da albarkatu da kayayyaki wajen raya tattalin arzikin kasar da inganta rayuwar al'ummarta. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China