in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Layin dogon da kasar Sin ta shimfida tsakanin Habasha da Djibouti ya samar da ci gaba tare da hade nahiyar Afrika
2018-06-16 17:22:19 cri
Jami'an Tarayyar Afrika AU da jami'an diflomasiyyar nahiyar, sun yabawa layin dogon da kasar Sin ta shimfida tsakanin Habasha da Djibouti, inda suka bayyana shi a matsayin aikin da ya taimakawa nahiyar cimma muradinta na samun ci gaba da kuma dunkulewar nahiyar.

Tawagar kasar Sin a AU ce ta shirya wani bulaguro da ya hada jami'an AU da sauran jami'an diflomasiyyar kasashen nahiyar, cikin jirgin kasan da ya hada Habasha da Djibouti.

Shugaban Tawagar ta kasar Sin Kuang Weilin, ya ce tafiyar wadda ta hada da ziyartar yankin masana'antu da kasar Sin ta gina a garin Adama dake da nisan kilomita 80 daga birnin Addis Ababa na Habasha, na da nufin ba matafiyan damar ganewa idonsu ayyukan da aka aiwatar karkashin hadin gwiwar kasar Sin da nahiyar Afrika da kuma shawarar 'Ziri Daya da Hanya Daya'.

A cewar Rossette Nyirinkindi Kataungye, mashawarcin AU kan hadin kan nahiyar, layin dogon misali ne na kudurin kasar Sin, na taimakawa nahiyar Afrika cimma burinta na samun ci gaba da kuma dunkulewa wuri guda. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China