in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kara hadin-gwiwa tsakanin kasashe maso tasowa zai taimaka ga warware matsalar mace-macen mata masu juna biyu da jarirai a Afirka
2018-08-17 21:06:50 cri
Yau Jumma'a, a birnin Beijing, aka bude wani dandalin tattaunawa mai taken "kara hadin-gwiwar Sin da Afirka a fannin kiwon lafiya don tabbatar da lafiyar iyaye mata da jariransu", wanda ya kasance wani muhimmin fanni na babban taron hadin-gwiwar Sin da Afirka a fannin kiwon lafiya na shekarar 2018.

Wakilai daga kasashen Afirka da kungiyar tarayyar Afirka wato AU da kuma kasar Sin sun yi kira da a karfafa hadin-gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, da zuba karin kudade, da kara mai da hankali wajen kula da lafiyar mata da yara kanana, ta yadda za'a rage yawan mace-macen jariran da aka haifa.

Wata babbar jami'a daga kwamitin kula da harkokin kiwon lafiya ta kasar Sin Madam Song Li ta ce, Sin na fatan yayata nasarorin da ta samu a fannin inganta lafiyar mata da yara kanana ga kasashen Afirka, a wani mataki na bayar da gudummawarta ga inganta lafiyar mata da yara kanana a fadin duniya baki daya. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China