in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojan kasar Sin ta ki yarda da wani rahoton da Amurka ta fitar game da ayyukan soja da yanayin tsaron kasar Sin
2018-08-18 15:45:29 cri
Ma'aikatar tsaron Amurka ta fitar da wani rahoto dangane da ayyukan soja da yanayin tsaron kasar Sin na bana, inda ta jirkita gaskiyar manufofin kasar Sin, da ikirarin cewa kasar Sin na kawo barazana ga ayyukan soji, tare kuma da bullo da wasu kalaman da ba su dace ba game da dangantakar dake tsakanin babban yankin kasar Sin da yankin Taiwan. Mai magana da yawun ma'aikatar tsaron kasar Sin, Wu Qian ya ce, rundunar sojan kasar ta ki amincewa da rahoton Amurka, haka kuma ta nuna matukar takaici game da shi.

Wu Qian ya jaddada cewa, kasar Sin ta dade tana neman samun ci gaba cikin lumana, da bayar da gudummawarta wajen tabbatar da zaman lafiya da tabbatar da kiyaye doka da oda a fadin duniya baki daya. Ya ce a 'yan shekarun nan, sojojin kasar Sin na nuna himma da kwazo wajen shiga ayyukan soja a kasashen waje, ciki har da kiyaye zaman lafiya, da bada kariya ga ayarin jiragen ruwa da kuma gudanar da ayyukan ceto. Kasar Sin na kara sauke nauyin dake wuyanta, da tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya, kuma gudummawa gami da kokarin da ta yi sun sa ta samu yabo daga kasashen duniya.

Bugu da kari, Wu ya jaddada cewa, Taiwan wani yanki ne da ba za'a iya raba shi daga kasar Sin ba. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China