in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ra'ayoyin jami'an Najeriya da Nijer game da taron kolin FOCAC na Beijing na 2018
2018-09-04 13:45:41 cri


A ranar 3 ga wannan wata na Satumbar shekarar 2018 ne, aka bude taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afrika wato FOCAC, wanda gwamnatin Sin ta karbi bakuncinsa a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, wakilin sashin Hausa na CRI Ahmad Inuwa Fagam ya samu zantawa da wasu daga cikin tawagar jami'an hukumomin gwamnati na kasashen Najeriya da Jamhuriyar Nijer da suka hada da gwamnonin jahohi, da ministoci da sauran jami'ai na bangarori daban daban, inda suka bayyana ra'ayoyinsu game da taron kolin FOCAC na Beijing da ma sauran batutuwa da suka shafi hulda tsakanin Sin da kasashen Afrika.

Barrista Abdullahi Abubakar, shine gwamnan jahar Bauchi a Najeriya, yana daga cikin gwamnonin da suka yi tattaki don halartar taron kolin FOCAC na Beijing, kuma ya bayyana taron da cewa yana da matukar tasiri ga ci gaban kasashen Afrika.

Shi ma Injiniya Sulaiman Adamu ministan albarkatun ruwa na Najeriya, ya ce taron FOCAC wata babbar dama ce ta yin hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika a matsayinsu na kasashe masu tasowa.

Usman Muhammad, shi ne babban sakataren ofishin hukumar cinikayya ta Jamhuriyar Nijer, ya ce taron kolin dandalin Sin da Afrika taro ne mai muhimmanci dake hada kan shugabannin kasashen Afrika, don tattaunawa da shugabannin kasar Sin, musamman yadda kasar Sin take nuna kauna ga kasashen Afrika, har ma ya bayyana fatan samun kyakkyawar dangantaka tsakanin kasar Sin da Jamhuriyar Nijer da ma kasashen Afrika baki daya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China