in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wa zai kawo barazana ga Taiwan?
2018-10-22 15:54:02 cri
A farkon watan da muke ciki ne, mataimakin shugaban kasar Amurka Mike Pence ya zargi kasar Sin da yin shisshigi cikin zaben Amurka, da kawo kalubale ga tsarin kasashen duniya, da kuma yin barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a zirin Taiwan.

A kwanakin baya, ba sau daya ba kuma ba sau biyu ba, rundunar sojan Amurka ita ma ta yi wasu kalamai dangane da batutuwan da suka shafi Taiwan. Babu shakka dukkan wadannan abubuwan da Amurka ta yi, za su yi illa ga dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka da kuma alakar dake tsakanin babban yankin kasar Sin da lardin Taiwan, har ma su kawo barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali. Amma irin martanin da hukumar Taiwan dake karkashin jagorancin Tsai Ing-wen ta mayar, za ta janyo hadari ga lardin Taiwan.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China