Shugaban kwamitin mai shari'a Clement Atangana, shi ne ya bayyana hakan yayin bikin fara bayyana sakamakon zaben, a birnin Yaounde fadar mulkin kasar.
Mr. Atangana ya ce za a fara ne da bayyana sakamakon zaben yankuna, da na sassa, da kananan sassan kasar. Sai kuma na kuri'un da aka kada a wajen kasar, kafin daga bisani a bayyana wanda ya lashe zaben baki daya.
Mai shari'a Atangana ya ce zaben ya cika sharuddan kasancewa mai inganci da tsafta, kuma kwamitin kundin mulkin kasar ya gamsu da shi.