in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi bikin tunawa da mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon kisan kiyashin da maharan Japan suka yi a Nanjing
2018-12-13 13:35:58 cri

Yau Alhamis, kwamitin tsakiya na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, da majalisar gudanarwar kasar sun gudanar da bikin tunawa gami da nuna jaje ga mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon kisan kiyashin da mahara Japanawa suka yi a birnin Nanjing dake gabashin kasar, a shekara ta 1937. Memba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana mataimakin shugaban majalisar wakilan jama'ar kasar Wang Chen ya gabatar da muhimmin jawabi a wajen bikin da ya samu halartar wakilai sama da dubu 8 daga bangarori daban-daban na kasar Sin.

Tun daga yau Alhamis, za'a soma aiwatar da dokar da ta amince da shirya bikin tunawa da mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon kisan kiyashin da maharan kasar Japan suka yi a Nanjing a hukumance, dokar da ta kasance irinta ta farko da kasar Sin ta zartas kan bikin tunawa da mutanen. Dokar ta tanadi yadda za'a tallafawa mutanen da suka tsallake rijiya da baya a kisan kiyashin da aka yi a Nanjing, da matakan kula da wuraren da ake shirya bikin tunawar

A ranar 27 ga watan Fabrairun shekarar 2014, a yayin taro karo na bakwai na zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 12, aka zartas da wata doka, inda aka kebe ranar 13 ga watan Disambar kowace shekara a matsayin ranar tunawa da mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon kisan kiyashin da maharan Japan suka aikata a birnin Nanjing.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China