in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya mika sakon taya murna ga taron "Fahimtar Sin" karo na uku
2018-12-16 20:04:49 cri
Yau Lahadi, aka bude taron "Fahimtar Sin" na kasa da kasa karo na uku a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika sakon taya murna don gudanarwar taron, ya kuma nuna maraba da zuwan wakilan siyasa, kamfanoni, da na masanan jami'o'i na kasa da kasa.

Xi Jinping ya ce, ana fuskantar sauye sauye a nan duniya, amma kawo yanzu, ba a canja babban burin neman ci gaba cikin zaman lafiya ba, a sa'i daya kuma, mutanen duniya suna fuskantar kulubaloli da dama. Kasar Sin tana son yin hadin gwiwa da kasa da kasa domin kafa dangantakar dake tsakanin kasashen duniya bisa ka'idojin girmama juna, nuna adalci, da yin hadin gwiwa da kuma cin moriyar juna, ta yadda za a kara dunkulewar dukkanin bil Adam, da kuma ba da gudummawa yadda ya kamata wajen kiyaye zaman lafiya da neman bunkasuwar kasa da kasa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China