Moussa Faki Mahamat, wanda ya bayyana damuwa game da asarar rayuka da aka samu a wasu yankunan kasar a lokutan yakin neman zaben, ya ce hakan na iya yin barazana ga nasarar zaben dake tafe. Don haka a cewar sa, ya kamata 'yan siyasa da sauran masu ruwa da tsaki, su rungumi akidar siyasa, su kuma tabbatar da gudanar zaben cikin lumana da adalci, kamar yadda dokokin zabe na kasashen Afirka, da ma na sauran kasashen duniya suka tanada.
Ya kuma nuna damuwa, game da konewar kayan zabe a birnin Kinshasa, sakamakon wata gobara da ta tashi a wani rumbun adana kayayyaki na hukumar zaben kasar, tsakanin ranekun 12 zuwa 13 ga watan nan.
Wata sanarwa da kungiyar AU ta fitar a jiya Lahadi, ta ce an samu asarar rayuka a yankunan Kalemie, da Lubumbashi da Mbuji-Mayi, yayin da ake daf da gudanar da babban zaben kasar na karshen mako.