Wata sanarwa da fadar shugaban kasar ta fitar a jiya Lahadi, ta ce an kori mai shari'a Ayisi Addo, da Uuter Paul Dery, da Mustapha Logoh daga aikin su ne, sakamakon shawarar kwamitin binciken zargin da aka yi musu. Kwamitin ya hakkake cewa, halayyar da alkalan suka nuna, ta sabawa dokokin kasar Ghana.
Babbar mai shari'a ta kasar Sophia Akuffo ce dai ta kafa kwamitin binciken, bayan da dan jaridar nan mai kwarmata bayanai Anas Aremeyaw Anas ya gabatar da korafi a kan su.
Alkalan uku dai na cikin jimillar alkalai 22, na manya da kananan kotunan kasar da aka zarga da aikata cin hanci da rashawa shekaru uku da suka gaba.