in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Saudiyya ta yi watsi da yunkurin majalisar dattijan Amurka game da mutuwar dan jarida
2018-12-17 15:38:56 cri
A yau Litinin gwamnatin Saudiyya ta yi watsi da yunkuri na baya bayan nan da majalisar dattijan Amurka ta yi game da mutuwar dan jaridar kasar Saudiyyan Jamal Khashoggi, kamfanin dillancin labarai na Saudi Press ne ya bada rahoton.

A ranar Alhamis majalisar dattijan Amurka ta kada kuri'ar neman a kawo karshen tallafin sojin da Amurka ke bayarwa ga dakarun hadin gwiwa dake yaki a Yemen wanda Saudiyya ke jagoranta, inda majalisar ta zargi yariman Saudi Mohammed bin Salman da hannu wajen mutuwar dan jaridar kasar Khashoggi.

Zargin da majalisar dattijan ta Amurka ke yi, "zargi ne marar kwararan hujjoji, kana zargi ne mai cike da yin shisshigi game da harkokin cikin gidan masarautar Saudiyya, da kuma neman zubarwa masarautar kima a idanun shiyyar da ma duniya bisa ga irin rawar da kasar ke takawa a matakin kasa da kasa," ma'aikatar harkokin wajen Saudi ce ta bayyana hakan cikin wata sanarwa. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China