in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU, da MDD sun damu game da halin da ake ciki a Mali
2019-02-21 10:52:28 cri
Rundunar wanzar da zaman lafiya ta MDD da kungiyar tarayyar Afrika (AU) sun bayyana damuwa game da halin tabarbarewar yanayin tsaro da ake ciki a tsakiyar Mali.

A wata sanarwar da AU ta fitar ta ce, rundunar tsaron hadin gwiwar ta bukaci gwmanatin Mali ta rubanya kokarinta wajen shawo kan tabarbarewar yanayin tsaron da ake fuskanta a kasar, tare da hadin gwiwar da masu tallafawa shirin wanzar da zaman lafiyar a kasar.

Hukukomin biyu sun yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su jajurce wajen tabbatar da ganin an dauki matakan aiwatar da yarjejeniyar hana yaduwar makamai da wayar da kan al'umma kan tabbatar da zaman lafiya.

Tawagar hadin gwiwar ta kara nanata kira ga kasa da kasa dasu tallafawa shirin hadin gwiwar na wanzar da zaman lafiyar na dakarun kiyaye zaman lafiya na MDD a Mali (MINUSMA).(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China