in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun adawa na kasar Sudan sun sanar da tsagaita bude wuta har zuwa karshen watan Yuli
2019-04-18 10:09:05 cri

Babbar kungiyar dakaru masu adawa ta kasar Sudan wato SPLM-North ta bayar da sanarwa cewa, tun daga nan zuwa ranar 31 ga watan Yuli na bana, kungiyar ta dakatar da aikin nuna adawa a yankunansu.

Sanarwar ta bayyana cewa, dakatar da aikin nuna adawar mataki ne da kungiyar SPLM-North ta dauka don daidaita batun kasar Sudan cikin lumana, hakan zai taimakawa mika ikon kasar ga gwamnatin fararen hula.

Sojojin gwamnatin kasar Sudan sun yi yake-yake da kungiyar SPLM-North tun daga shekarar 2011. A watan Yuni na shekarar 2016, shugaban kasar Sudan na lokacin Omar al-Bashir ya sanar da cewa, sojojin gwamnatin kasar sun tsagaita bude wuta har na tsawon watanni 4. Bayan hakan, gwamnatin kasar Sudan ta tsawaita wa'adin tsagaita bude wuta a yankunan dake tinkarar rikice-rikice sau da dama. Kana kungiyoyi masu adawa da dama su ma sun sanar da tsagaita bude wuta a kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China