in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Kasar Sin: Shawarar Ziri Daya da Hanya Daya sabon karfin dake ingiza huldar Kasar Sin da Habasa
2019-04-19 10:30:54 cri
Jakandan Kasar Sin a Habasha Tan Jian, ya ce shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da kasar Sin ta gabatar, na zaman sabon karfin dake ingiza hulda tsakanin kasar Sin da Habasha.

Da yake jawabi ga manema labarai a harabar ofishin jakadancin kasar Sin dake birnin Addis Ababa, Tan Jian ya ce taro kan shawarar Ziri Daya da Hanya Daya domin hadin giwar kasa da kasa da zai gudana a karshen watan nan a Kasar Sin, wani karfi ne da zai kara karfafa kawance tsakanin kasahsen biyu.

Ya ce hadin gwiwa kan shawarar ba zaman muhawara ba ce, yana mai cewa shiri ne da ya fi mayar da hankali kan aiwartar da ayyukan dake haifar da kyawawan sakamako. Ya ce bangarorin da za su halarci taron za su dora ne a kan nasarorin da aka samu, tare da kirkiro wasu ayyukan karkashin hadin gwiwar a matakai daban daban da za su kawo karin sakamako masu inganci.

Tan Jian ya ce Habasha na daya daga cikin kasashe 124 da suka sanya hannu kan hadin gwiwa da kasar Sin karkashin shawarar, ya na mai jaddada kudurin kasar Sin na marawa Habasha baya wajen taka muhimmiyar rawa a fannin yayata shawarar a nahiyar Afrika.

Jakadan ya kuma bayyana cewa, hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Habasha za ta ci gaba da bunkasa tare da zama abun koyi a tsarin shawarar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China