Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Bikin CIIE ya samar da dandalin muamala ga kasashen Afirka
2019-11-11 10:42:55        cri

Jiya Lahadi, aka rufe bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin wato CIIE karo na biyu a birnin Shanghai na kasar Sin. Wasu shugabanni da masana na kasashen dake gabashin nahiyar Afirka suna ganin cewa, bikin baje kolin CIIE ya samar wa kasa da kasa muhimman dandalin nuna kayayyakinsu da kuma yin mu'amala.

Shugaban kasar Ruwanda Paul Kagame ya bayyana cewa, a halin yanzu, ana fuskantar sauyin yanayi ta fuskar ciniki a duniya, kasar Ruwanda tana son hadin gwiwa da kawancen dake hada wasu kasashe, ko kuma yin hadin gwiwa da babbar kasa mai samun ci gaba a fannin tattalin arziki kamar kasar Sin. Kuma yana fatan kara moriyar da kasar Ruwanda da sauran kasashen Afirka za su samu, ta hanyar halartar bikin baje kolin CIIE da kasar Sin ta kira.

Haka kuma, masanin kasar Kenya Stephen Ndegwa ya gabatar da sharhi mai taken "A ganin kasar Kenya, kasuwanni a kasar Sin suna da kyau". Cikin sharhin, ya ce, kasar Sin ita ce babbar abokiyar ciniki ta kasar Kenya, kana, kasar Kenya ta sami gabilin jarin waje daga kamfanonin kasar Sin. Ko da yake, tana fuskantar rashin daidaito ta fuskar ciniki a tsakaninta da kasar Sin, amma, za ta warware wannan matsala ta hanyar kara fitar da hajoji zuwa kasar Sin, a maimakon, rage hajojin da za ta shigar kasar daga kasar Sin. Haka kuma, ya ce, bikin baje kolin CIIE ya samar wa kasar Kenya wata kyakkyawar dama wajen habaka kasuwannin kasar Sin masu kunshe da mutane biliyan 1.4. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China