2019-11-16 17:05:37 cri |
Jawabin Shugaba Xi Jinping ya bayyana ainihin gaskiyar lamuran da ke faruwa a Hong Kong da ma illolin da suka haifar, ya kuma bayyana matsayin gwamnatin kasar Sin na goyon bayan hukumar yankin musamman na Hong Kong wajen daidaita batun yankin bisa doka, baya ga haka, ya kuma bayyana niyyar gwamnatin kasar Sin ta kiyaye ikon kasar. Wannan shi ne karo na farko da shugaban kasar Sin ya yi jawabi a fili dangane da rikicin Hong Kong da illolinsa da ma matsayin gwamnatinsa da niyyarta, ya kuma isar da sako ga kasa da kasa a kan batun.
Batun Hong Kong harka ce ta cikin gidan kasar Sin, kada kuma a raina wa niyyar kasar Sin ta kiyaye ikonta da ma tsaronta da ci gabanta, kada kuma a gurgunta fahimtar sakwannin da gwamnatin kasar Sin ta samar kan batun Hong Kong. (Lubabatu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China