2019-11-17 20:23:51 cri |
An yi nuni da cewa, masu tsattsauran ra'ayi sun keta tsarin dokoki da odar zamantakewar al'umma, tilas ne a yanke hukunci gare su. Sun tuntubi kungiyoyin kasashen waje masu kin amincewa da Sin da keta mutuncin kasar da ka'idojin tsarin kasa daya amma da tsarin mulki biyu, wanda kowace kasa ba za ta amince da shi ba.
An kara da cewa, wannan ne karo na farko da shugaban kasar Sin ya yi bayani game da babbar illa da ayyukan masu tsattsauran ra'ayi suka kawo wa yankin Hong Kong, da gabatar da aikin dakatar da ayyukan da mayar da doka da odar yankin, wanda ya shaida hanyar da za a bi don tabbatar da tsaron yankin Hong Kong. (Zainab)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China