Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Akwai yiwuwar Farin Hamada na Desert locusts su tunkari kasashen Uganda da Sudan ta Kudu da Habasha
2020-01-25 16:48:18        cri
Akwai yiwuwar Farin Hamada da ake kira Desert Locusts da suka addabi kahon Afrika, su koma kasashen Uganda da Sudan ta Kudu da kuma kudu maso yammacin Habasha.

Stephen Njoka, Darakta Janar na hukumar yaki da kwari ta gabashin Afrika, ya ce kwarin da aka samu rahoton ganinsu a arewacin Kenya a watan Disamban bara, na tunkarar yankunan Baringo da Turkana na kudu maso yammacin Kenya.

Ya ce hadarin bazuwarsu zuwa kasashen 3 na da karfi sosai, la'akari da karancin ayyukan yaki su a wasu kasashen, da kuma yadda suke da karfin tafiya da hayayyafa.

Jami'in ya ce, hukumar da abokan huldarta a shirye suke, kana suna da isassun magungunan feshin kwari da jiragen domin yaki da kwarin masu saurin tafiya.

A nasa bangaren, mataimakin Darakta Janar na hukumar samar da abinci da kula da aikin gona na MDD, kuma wakilin hukumar a nahiyar Afrika, Bukar Tijjani, ya ce shigowar kwarin na barazana ga wadatar abinci da rayuwar jama'a a yankin gabashin Afrika. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China