Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Dalilin da ya sa aka ga bayan COVID-19 a birnin Wuhan
2020-05-08 21:12:53        cri

A kwanakin baya, Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta yi maraba da labarin dake cewa, babu wani mai dauke da cutar COVID-19 dake kwance a asibitin birnin Wuhan na kasar Sin, inda ta jinjinawa namijin kokarin da kasar ta yi wajen dakile annobar.

Bayan shafe sama da watanni 3 ana yaki da cutar, yanzu a birnin Wuhan dake yankin tsakiyar kasar Sin, da ya taba kasancewa inda cutar COVID-19 ta fi kamari, an sallami dukkan wadanda suka kamu da cutar COVID-19 dake kwance a asibiti, bayan sun warke, to, sai dai mene ne dalilin da ya sa ake samun wannan nasara a birnin. Sani Ibrahim, dalibi dake karatun digiri na 3 a birnin zai yi mana karin bayani dangane da batun.

 


 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China