2020-07-02 20:17:18 cri |
Zhao ya kara da cewa, harkokin Hong Kong, ciki har da batun kafuwar dokar tsaron kasa mai nasaba da yankin na Hong Kong, wasu ayyuka ne na cikin gidan kasar Sin, don haka wata kasar waje, ba ta da hurumin tsoma baki ciki. Ya ce yunkurin kasar Amurka na neman hana kasar Sin aiwatar da dokar tsaron kasa da ta shafi Hong Kong ba zai yi nasara ba.
A nasa bangare, kwamiti mai kula da harkokin waje, na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, shi ma ya ba da wata sanarwa a yau Alhamis, inda ya yi Allah wadai, da mummunar dokar da kasar Amurka ta zartas. (Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China