2020-07-03 19:41:36 cri |
Cikin wadannan kasashe, Burundi ta yabawa kasar Sin, game da kokarinta a fannin kare hakkin dan Adam, da gudunmowar da kasar ta Sin ta samar ta fuskar kare hakkin bil Adama a duniya. A cewar kasar, kafuwar dokar tsaron kasa mai nasaba da yankin Hong Kong, za ta taimaka wajen kare hakkin dan Adam a yankin.
A nata bangaren, kasar Kamaru ta nuna kin amincewa da yadda wasu kasashe suke amfani da batun Hong Kong, da na Xinjiang, wajen tsoma baki cikin harkokin gidan kasar Sin.
Sa'an nan kasashen da suka hada da Najeriya, da Aljeriya, da Morocco, sun bayyana cewa, ya kamata a girmama wasu manyan ka'idojin da ake bi wajen kula da huldar kasa da kasa, maimakon fakewa da batun hakkin dan Adam, don neman yin shisshigi cikin harkokin gidan wata kasa. (Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China