2020-07-07 20:41:13 cri |
Bugu da kari, matakin ya alamta kudirin kasar na goyon bayan tsarin kasancewar bangarori daban-daban, da kiyaye tsarin makamai na kasa da kasa, da gudanar da tsarin gina al'umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bil-Adam.
A jiya ne zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Zhang Jun, ya gabatar da bukatar kasarsa na shiga yarjejeniyar cinikayyar makamai ga babban sakataren MDD a hedkwatar majalisar. Zhang Jun ya ce, matakin na kasar Sin, shi ne cikamakin dukkan ka'idojoji na doka dake baiwa kasar damar shiga wannan yarjejeniya, wadda za ta fara aiki cikin kwanaki 90 daga jiyan.(Ibrahim)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China