Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasar Sin ta yi bikin cika shekaru 83 da yakin al'ummarta kan maharan Japanawa
2020-07-07 21:00:35        cri
A yau Talata ne, kasar Sin ta shirya wani biki a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, don tunawa da cika shekaru 83 da yadda baki dayan al'ummar kasar suka nuna turjiya ga yakin Japanawa.

Ana dai daukar abin da ya faru a ranar 7 ga watan Yulin shekarar 1937 a gadar Logou, a matsayin mafarin hare-haren da Japan ta yiwa kasar Sin, kuma baki dayan al'ummar kasar suka nuna turjiya.

Lamarin na ranar Talata ya faru a kusa da gadar, a dakin ajiye kayan tarihi na yakin al'ummar Sinawa kan maharan Japanawa.

Sama da mutane 200, ciki har da mambobin iyalan shugabannin sojoji da wadanda suka yi shahada a yaki ne, suka halarci bikin.

Mutane sun ajiye furanni tare da sunkuyawa don nuna gimamawa ga wadanda suka mutu a yakin kin kutsen Japanawa da ya faru sama da shekaru 80 da suka gabata.

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China