2020-08-04 10:56:23 cri |
Kamfanin dillancin labarai na APS ya ruwaito shugaban na bayyana haka ne yayin taron majalisar tsaro da ya samu halartar manyan jami'an soji da sauran jam'an tsaro, tare kuma da ministoci, domin nazartar yanayin annobar COVID-19 a kasar.
Shugaba Tebboune ya umarci Firaminista Abdelaziz Djerad, ya shirya bude masallatan sannu a hankali.
Ya kara da cewa, da farko, shirin zai bude manyan masallatai 1,000, wanda zai bada damar bayar da tazara tsakanin mutane, sannan dole ne kowa ya sanya makarin baki da hanci. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China