Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Ministan harkokin wajen Najeriya ya warke daga COVID-19
2020-08-13 09:38:55        cri

Rahotanni daga Najeriya na tabbatar da cewa, ministan harkokin wajen kasar Geoffrey Onyeama, ya warke daga cutar numfashi ta COVID-19, bayan kebe kansa na makonni uku.

Ministan wanda aka tabbatar ya kamu da cutar a ranar 19 ga watan Yulin da ya gabata, ya wallafa a shafinsa na twita cewa, sakamakon gwaji na baya-bayan aka yi masa bayan killace kansa na tsawon makonni uku, ya nuna cewa, ya warke daga cutar.

A don haka kamar yadda waccar kafa a baya ta sanar da cewa, ya kamu da cutar COVID-19 a watan da ya gabata, yanzu ba ya dauke da kwayar cutar. (Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China