2020-08-18 11:32:20 cri |
Kakakin rundunar John Enenche, ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, an lalata maboya da cibiyar gudanar da ayyukan kungiyar dake yankunan Tumbuma Baba da Boboshe dake jihar.
Luguden wutan ya biyo bayan sahihan bayanan sirri game da ayyukan mayakan da kuma ayyukan sa ido da aka gudanar, wadanda suka nuna adadi mai yawa na 'yan ta'addan a yankunan, da wajen adana kayayyakinsu da wajen da suke gudanar da taruka,
Kakakin ya ce rundunar za ta ci gaba da kokarinta na kawar da 'yan ta'adda da sauran masu aikata laifuffuka a yankin mai fama da rikici. (Fa'iza Mustapha)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China