Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasar Sin ta bayyana kudurinta na ci gaba da zurfafa alaka da Morocco
2020-08-24 14:08:08        cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana kudurin kasarsa na ci gaba da zurfafa hadin gwiwa bisa manya tsare-tsare da kasar Morocco. Da ci gaba da taimakawa kasar Morocco a yaki da cutar COVID-19 gami da kokarin dawo da harkokin samar da kayayyaki.

Mr. Wang wanda ya bayyana haka kwanakin baya, yayin zantawa da takwaransa na kasar Morocco Nasser Bourita ta wayar tarho, ya ce, hadin gwiwar kasashen bisa manyan tsare-tsare karkashin jagorancin shugaba Xi Jinping na kasar Sin da Sarki Mohammed VI na Morocco, ta jure tasirin annobar COVID-19, har ta kara bunkasa.

Ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da taimakawa kokarin kasar Morocco na yaki da annobar CIVID-19, tare da dawo da harkokin tattalin arziki, da rawar da kasar ke takawa a harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya.

Wang ya yi nuni da cewa, da zarar kasar Sin ta yi nasarar samar da riga kafin COVID-19, har aka fara amfani da ita, duniya da kasashen Afirka na daga cikin wadanda za su fara amfana.

A nasa bangare Bourita, ya bayyana cewa, kwarewar da kasar Sin ta samu a fannin yaki da COVID-19, ta taimakawa kasarsa, kuma Moroccon na da tabbaci kan fasahar kasar Sin a fannin samar da riga kafi. A don haka, Morocco tana fatan nan ba da dadewa ba, sassan biyu za su sanya hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa a tsakaninsu. (Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China