A yau ne Xi Jinping, babban sakataren kwamitin koli na JKS, ya jagoranci wani taron da hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS ta kira, inda aka yi bitar wani tsari game da kare muhallin halittu da kara bunkasa yankin Rawayen kogi, gami da rahoton da kwamitin koli na JKS na 19 ya gabatar kan zagaye na biyar na aikin sanya ido da ladabtarwa. (Ibrahim)