Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Hukumar FA a Ghana ta gudanar da taro gabanin fara buga sabuwar kakar wasa
2020-09-02 09:56:09        cri

Hukumar wasan kwallon kafar ta kasar Ghana ko GFA, ta gudanar da taron gama-gari karo na 26, domin nazarin batutuwa masu nasaba da kakar wasa ta 2019 zuwa 2020 da aka soke, sakamakon bullar cutar COVID-19, da kuma tabbatar da lokacin fara bude sabuwar kakar wasa.

Shugaban hukumar ta GFA Kurt Okraku, ya yi kira da a samar da hadin kai tsakanin 'yan kwallo da sassan masu ruwa da tsaki, domin inganta harkar wasan a kasar. Mr. Okraku ya ce, kwallon kafa na da matukar karbuwa a Ghana, kuma wasa ne daya tilo dake hade kan al'ummar kasar, don haka ya zama wajibi, a yi aiki tukuru wajen habaka shi, ta yadda zai samar da wadata ga kowa.

Jami'in ya kara da yin kira ga dukkanin sassa, da su hada karfi da karfi wajen gina wasan kwallo mai nagarta a kasar.

Muhimman kudurori da aka tattauna kan su yayin taron na GFA, sun hada da batun kakar shekarar 2019-20 da aka soke, bayan bullar cutar COVID-19. Kana an amince da bude sabuwar kakar wasa ta 2020 zuwa 2021 a watan Oktoba dake tafe, muddin dai gwamnatin kasar ta dage dakatarwar da ta yiwa harkokin wasannin kasar. (Saminu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China