Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Nijer zata shugabanci kwamitin sulhun MDD a wannan wata na Satumba
2020-09-02 11:08:49        cri
Jamhuriyar Nijer, dake shiyyar yammacin Afrika, ta karbi shugabancin kwamitin sulhun MDD a watan nan na Satumba, a lokacin da aka kaddamar da fara babban taron MDD karo na 75.

A cewar rahoton kwamitin sulhun MDD, an zabe Nijer domin ta jagoranci taruka 4 wadanda zasu bayar da fifiko kan wasu muhimman bangarori, manufar hakan shi ne, domin aiwatar da tsarin ayyukan kwamitin sulhun bisa gaskiya da inganci.

Jadakan jamhuriyar Nijer a MDD yace, hakika, tsarin diflomasiyya shine lalibo hanyoyin daidaita al'amurra, jakadan ya amsa tambayoyi da suka hada da batun hadaddiyar yarjejeniyar nan ta JCPA, wato yarjejeniyar nukiliyar Iran, ita dai wannan yarjejeniyar ta shirin makaman Iran wacce aka cimma matsaya kanta a birnin Vienna a ranar 14 ga watan Yulin shekarar 2015, tsakanin kasar Iran da wakilan mambobin kasashe 5 masu kujerun dindindin a MDD da suka hada da Sin, Faransa, Rasha, Birtaniya da Amurka sai kuma Jamus da kungiyar tarayyar Turai. (Ahmad)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China