Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Xi ya isar da sakon gaisuwa ga malamai gabanin bikin ranar malamai ta kasa
2020-09-09 13:39:46        cri
Shugaban kasar Sin, wanda ila shi ne babban sakataren kwamitin koli na JKS, kana shugaban rundunar sojojin kasar Xi Jinping, ya aika da sakon gaisuwa ga malamai da ma'aikatan dake aiki a sashen Ilimi a sassan kasar, gabanin ranar malamai ta kasar Sin da za a yi bikin ta a gobe Alhamis 10 ga watan Satumba.Xi ya ce, a yayin da aka samu bullar cutar COVID-19 ba zato ba tsammani, malamai a sassan kasar Sin sun jure duk wasu matsaloli, inda suka ci gaba da aiki tare da ba da muhimmiyar gudummawa a yaki da wannan annoba, ta hanyar sadaukar da kai wajen koyarwa ta kafar Intanet da ya karade duniya.Shugaba Xi ya bukaci a kara kula da malamai,inda ya jaddada muhimmancin martaba aikin malamanta a cikin al'umma, da hada matakan yaki da COVID-19 da aikin samar da Ilimi yadda ya kamata.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China