2020-09-16 15:56:17 cri |
A wajen wani taron manema labaru, Meng ta ce, a ranar 9 ga wata, kungiyar 'yan kasuwan kasar Amurka dake birnin Shanghai na kasar Sin, ta gabatar da wani rahoto, inda ta ce yawancin mambobin kungiyar suna sa ran ganin karuwar kasuwannin kasar Sin, kana kashi 78.6% daga cikin kamfanonin da suka halarci bincike sun ce ba za su janye jiki daga Sin ba.
Sa'an nan a ranar 10 ga wata, kungiyar 'yan kasuwan kasashen Turai dake kasar Sin ta gabatar da wani rahoto dake cewa, kashi 11% na kamfanonin Turai ne kawai ke da shirin sauya tsarinsu na zuba jari a kasar Sin.
Wadanna alkaluma, a cewar Madam Meng, sun nuna cewa, kamfanonin kasashen waje suna da imani sosai kan ci gaba da zuba jari ga kasar ta Sin. (Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China