Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Yang Jiechi zai halarci taron manyan jami'an BRICS karo na 10 kan batutuwan tsaro
2020-09-16 19:48:29        cri

A gobe Alhamis ne, mamban hukumar siyasa ta kwamitin koli na JKS, Yang Jiechi zai halarci taron manyan wakilan BRICS karo na 10 kan batutuwan da suka shafi tsaro.

Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Wang Wenbin, wanda ya bayyana haka yayin taron manema labarai da aka shirya, ya bayyana cewa, Yang, wanda har ila shi ne, darektan ofishin hukumar kula da harkokin waje ta kwamitin koli na JKS, zai halarci taron da zai gudana ta kafar bidiyo ne, bisa gayyatar sakataren hukumar tsaron kasar Rasha, Nikolai Patrushev. (Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China